15/03/2026
Assalamualaikum warahmatullahi wabarakatu
Tunatarwa Mai mahimmanci ga yan'uwa Musulmai. Sallah Edi na gabatowa "HADITH Daga manzon Allah sallallahu alaihi wasallam yace mu wasa abun yankanmu Dan mu hutar da abunda zamu yanka " HADITH Daga manzon Allah sallallahu alaihi wasallam yace an-azabtar dawata mata akan mage ta daureta ba abinci harta mutu" Sabida haka yan'uwa musani akwai Hisabi stakanin mutane da Dabba awannan lokacin dayake gabatowa wasunmu mukankai ma masu aikin "KAJI" su yanka su gyara Amma abun lura zaka kasa gane yankawanne ke kashesu koh ruwan Zafin da'ake sasune ke kashe za'a yanka kaje sana magagin mutuwa za'a jefasu cikin ruwan zafi Allah zai tanbayemu. Sabida haka Dan Allah ga Wanda zasukai amusu aikin ko su zasuyi idan anyanka abun yanka atabbatar daya gama mutuwa kafin sashi cikin ruwan zafi. idan ma kaje kaga da layi ko yankawan kastaya kaga yanda zasu yanka kafin kawuce. Allah yasa mudace Allah yakarbi ibadanmu 🤲